loading-texture
MURYOYIN DA BA A SAURARA BA
Waɗannan labarai na ɗauke ne da cikakkn bayani game da musgunawa da tashin hankali da cin zarafin da ya shafi sad
Domin kara fahimtar matsalar, sai kukunna sauti.
0

MayakanBoko Haram sun kai farmaki a garinmu, wanda ya tilasta mu yin hijira. Na koma sansanin ‘yan gudun hijira na Bakassi tare da iyalina a shekarar 2016. Jim kaɗan bayan mun zauna a wannan wuri, sai tsohon mijina ya sanar da mahaifina cewa yana son ya sake aure na, (karo na biyu). Mahaifina kuwa ya aminta. Daga nan ya sake aurena. A lokacin ina ‘yar shekara 14.

https://www.unfpa.org/ha/unheardvoices/zainab
Danna ka saurara

MayakanBoko Haram sun kai farmaki a garinmu, wanda ya tilasta mu yin hijira. Na koma sansanin ‘yan gudun hijira na Bakassi tare da iyalina a shekarar 2016. Jim kaɗan bayan mun zauna a wannan wuri, sai tsohon mijina ya sanar da mahaifina cewa yana son ya sake aure na, (karo na biyu). Mahaifina kuwa ya aminta. Daga nan ya sake aurena. A lokacin ina ‘yar shekara 14.

Yayin da nake tare da iyayena, ban kasance ina samun duk abin da nake so, duk da haka ina da ‘yanci.

Na yi da-na-sanin yin aure da wuri. Idan na ga ‘yan mata da ba su yi aure ba, nakan ji ɓacin rai. Amma nakan yi musu murnar cewa a ƙalla ba su da wani nauyi a kawunansu. Idan na kalli ‘ya’yana, nikan ji dama-dama, suna sa in ji farin ciki.

story-letter
*An canza sunan domin matsalar tsaro

Matada ke rayuwa a sansanonin‘yan gudun hijira sun kasance cibiyar da munanan aikin cin zarafin jinsin bil Adama kan fadawa.

A TSAWATA. A DAINA CIN ZARAFIN JINSI
WANDA YA ƊAUKI HOTUNA SHI NE: Etinosa Yvonne